News
Masu motocin bos na haya sun fara yajin aiki a Legas
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
A yau ne al’ummar jihar Legas a kudu maso yammacin Najeriya suka wayi gari da matsalolin rashin motocin haya, tun bayan da masu motocin bas suka shiga yajin aikin gargadi na tsawon kwana bakwai a fadin jihar.
Direbobin motocin haya dai na zargin ma’aikatan karbar haraji na motocin haya da aka fi kira Agbero, da karbar kudi fiye da ƙima da sunan haraji daga direbobin.
Buhari ya taya Sabon Shugaban Brazil murna
Sun yi barazanar shafe tsawon kwana biyar zuwa bakwai suna yajin aiki, idan har gwamnatin jihar ba ta kakkaɓe hannun Agbero daga kan tituna da sunan karbar haraji daga motocin bas a jihar ba.
Da yawa daga titunan jihar sun kasance fayau babu alamar motocin bas na haya, sa’ilin da fasinjoji suka zama abin tausayi, inda masu motocin ne kadai ke kaiwa da komowa.
Dubban fasinjoji ne suka cika a kan manya da ƙananan titunan birni da kewayen jihar Legas.
Tuni al’ummar jihar suka fara ji a jikinsu sakamakon wannan yajin aiki da direbobin motocin hayar suka fara daga yau Litinin.
Wasu daga cikin fasinjoji sun yi amfani da duk wata kafa da ta rage mu su domin zuwa wuraren aiki ko kasuwanci, inda wasu suka hau motocin titiri wasu kuma suka samu tallafi daga motocin da ba na haya ba zuwa guraban harkokinsu. Wasu kuwa sun hakura sun koma gida.
Direbobin dai sun alakanta mambobin Agbero da zargin tursasawa da karbar wadannan kudade cewa akwai hannun kungiyar masu daukar ma’aikatan motocin haya ta (RTEAN) da kuma kungiyar NURTW da hannu a ciki.
Wasu daga cikin direbobin dai sun bayyana rashin jin dadinsu da matakan mambobin kungiyoyin kula da tashoshin.
-
News16 hours ago
Jam’iyyar Labour Party Ta Yi Alkawarin Kafa Hukumar Kula Da Hayar Gidaje A Kano
-
News3 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News6 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
