Connect with us

News

‘Bam’ Ya Kashe Mutum 2 A Kaduna 

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Wasu mutum biyu sun mutu yayin da wani abu da aka binne ya fashe ya kuma tashi da su a Karamar Hukumar Chikun ta jihar Kaduna.

Advertisement

 

Lamarin ya faru ne da misalin karfe 2:00 na yammacin Alhamis.

Advertisement

Mun Lalata Haramtattun Matatun Mai Sama Da 70 Cikin Mako 2 – Sojoji

 

Advertisement

Motar wadanda abin ya rutsa da su ta bi ta kan abin fashewar da ake zargin ’yan ta’adda ne suka dasa a Zangon Tofa a yankin Kabrasha.

 

Advertisement

Aminiya ta rawaito cewa mutanen kauyen na jigilar amfanin gonar da suka girbe lokacin da lamarin ya afku.

 

Advertisement

Kwamishinan Tsaro da Al’amuran Cikin Gida na Jihar Kaduna, Samuel Aruwan, yayin da yake tabbatar da faruwar lamarin, ya ayyana mutum biyu a matsayin wadanda suka rasa rayukansu; Babajo Alhaji Tanimu da Safiyanu Ibrahim.

 

Advertisement

A cewarsa, Gwamnatin Jihar na bincike kan lamarin.

 

Advertisement

Ya kuma ce Gwamnan Jihar, Nasiru El-Rufai, ya jajanta wa iyalan wadanda abin ya shafa.

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending