Connect with us

News

Air Peace Ya Dakatar Da Jigilar Zuwa Dubai Saboda Hana ‘Yan Najeriya Biza

Published

on

Air Peace

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Kamfanin Jiragen Sama na Air Peace ya dakatar da zirga-zirgar jiragensa zuwa birnin Dubai na Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), saboda hana ’yan Najeriya biza.

Advertisement

Sarkin Saudiyya ya ba da umarnin yin sallar roƙon ruwa a masallatan ƙasar

Aminiya ta ruwaito yadda hukumomin Hadaddiyar Daular Larabawa suka sanya dokar hana ‘yan Najeriya biza makonni uku da suka gabata.
saboda rashin iya mayar da kudaden tikitin baya ga raguwar fasinjojin da suka yi yunkurin zuwa Dubai.

Advertisement

Kamfanin na Air Peace, ya ce zai dakatar da aiki daga ranar Talata, 22 ga Nuwamban 2022, har sai lokacin da ya fitar da sabuwar sanarwa.

A cikin wata sanarwa da kamfanin ya fitar, ya ce, “Hakan ya biyo bayan ci gaba da rashin bai wa matafiya ‘yan Najeriya biza da Gwamnatin Hadaddiyar Daular Larabawa ke yi da kuma matsalolin da ke biyo baya.

Advertisement

“Air Peace yana aiki da Hadaddiyar Daular Larabawa kan dokar hana tafiye-tafiye na kasar kwanan nan, amma idan aka yi la’akari da matsalolin da matafiya na Najeriya ke fuskanta wajen shiga kasar, ya zama wajibi mu dakatar da ayyukanmu zuwa wani lokaci. Za mu bayar da sabuwar sanarwa nan gaba.

“Fasinjojin da wannan lamari ya shafa za su iya aike mana da korafinsu don ba su kulawar da ta dace.”

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending