Sports
Ko kun san nawa duk tawagar da ke gasar kofin duniya ta Qatar za ta samu?
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
A bana, hukumar kula da kwallon kafa ta duniya FIFA ta kara yawan kudin kyautar da ake bai wa kasashen da suka samu gurbin buga gasar lashe kofin duniya da ke gudana a kasar Qatar, da dala miliyan 40 maimakon dala miliyan dari 400 da ake kashewa.
Tun a watan Afrilun wannan shekarar ne dai hukumar ta FIFA ta sanar da bai wa kasashen da suka samu gurbin buga gasar dala miliyan daya da rabi don shirya wa gasar.
Wata kungiyar Saudiyya ta yi wa Ronaldo tayin kwantiragin Fam miliyan 300
Haka nan kowace tawagar kasar da ta halarci gasar ta bana cikin 32 sai da aka ba su dala miliyan 9 a matsalin kudin rukuni.
Duk wata kasa da ta samu damar tsallakawa zuwa zagaye na biyu na kasar, za ta samu dala miliyan 13, inda a jimillance kasashe 16 za su raba dala miliyan dari da hudu.
Sai matakin zagayen dab da na kusa dana karshe wato quarter-finals, inda kasashe 8 da suka kai wannan mataki za su samu dala miliyan 68, inda kowaccen su za ta samu dala miliyan 17.
Hakuma fri hausa ta rawaito cewa Kasar da ta kare a mataki na hudu za ta samu dala miliyan 25, sai kuma wacce ta kare a mataki na uku za ta samu dala miliyan 27.
Haka nan hukumar FIFA ta ware kyautar dala miliyan 30 ga duk kasar da ta kare a mataki na 2.
Duk kasar da ta samu nasarar lashe gasar ta bana kuwa zata samu zunzurutun kudi har dala miliyan 42.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
