Connect with us

News

Gwamnoni sun maida wani martani, bayan Buhari ya zarge su da sace kudaden ƙananan Hukumomi.

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

A daren jiya ne Gwamnonin suka yi wani taro domin domin fitar da kansu daga zargin

 

Advertisement

A daren jiya ne Gwamnonin suka yi wani taro domin domin fitar da kansu daga zargin shugaban kasa Muhammadu Buhari na wawure kudaden kananan hukumomi.

Zargin N5.6bn: Buhari Ya Sallami Shugaban NIRSAL

Idan dai ba a manta ba, Shugaban kasar ya bayyana a wani taro daban-daban cewa gwamnonin sun yi wa kananan hukumomin kasar zagon-kasa, wadanda a lokuta da dama ya zarge su da karkatar da kuɗaɗen su daga asusun tarayya.

Advertisement

 

Shugaban ya sake nanata zargin ne a jiya a wani taron da aka shirya wa mambobin babbar kwas na 44 (2022) na Cibiyar Nazarin Siyasa da Dabaru ta Kasa, NIPSS, a fadar shugaban kasa, Abuja.

Advertisement

 

Sai dai gwamnonin da suka mayar da martani game da zargin da shugaban kasar ya yi a jiya, sun ce ba sa cikin masu karkatar da kudaden kananan hukumomi.

Advertisement

 

Wadanda suka mayar da martani sun hada da gwamnan jihar Benue, Samuel Ortom; David Umahi na jihar Ebonyi; AbdulRahman AbdulRazaq na Jihar Kwara; Solomon Lalong na jihar Filato; Dapo Abiodun na jihar Ogun da Nyesom Wike na jihar Ribas

Advertisement

 

Kokarin da aka yi na ganin wasu gwamnonin su mayar da martani a lokacin manema labarai a daren jiya, amma bai haifar da sakamako ba.

Advertisement

 

Da yake jawabi a wajen taron, shugaba Buhari ya bayar da misali da wani abin da ya faru da wani gwamna da ba a bayyana sunansa ba, domin ya bayyana yadda wasu gwamnonin ke tafka almundahana wajen rabon kayayyakin da aka tanada domin gudanar da aikin kananan hukumomi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending