Connect with us

News

INEC ta gargaɗi masu son sayen ƙuri’u a zaɓukan Najeriya na 2023

Published

on

DAGA MARYAM BASHIR MUSA 

 

 

 

Hukumar zaɓe mai zaman kanta a Najeriya ta ja kunnen ƴan ƙsar da su guji saye da sayar da ƙuri’a a yayin zaɓukan da ke tafe a farkon shekarar 2023.

 

Advertisement

Jaridar Daily Post ta intanet da ta ruwaito INEC a yau, ta ce duk wanda aka kama da laifin zai fuskanci ɗaurin shekara guda a gidan yari da kuma biyan tarar naira 500,000.

Sojoji uku sun mutu bayan da jirginsu ya kama da wuta a Nijar

Wannan gargaɗi na zuwa ne bayan koke-koken da jama’a suka yi na zargin cewa ƴan siyasa na son sayen ƙuri’u a zaɓukan da ke tafe.

 

INEC na cikin matsin lambar ganin ta gudanar da sahihin zaɓe marar maguɗi da hana sayen ƙuri’un mutane – wanda yana cikin dalilan da suka sa babban bankin ƙsar ya ce ya ɗauki matakin sauya kuɗaden naira da rage yaɗuwar sabbin kudin don hana wannan ta’asa.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending