Connect with us

News

Gobara Ta Kone Gidan Kwamishina

Published

on

DAGA MARYAM BASHIR MUSA

 

 

Gobara ta kone gidan Kwamishinan Harkokin Gona na Jihar Ogun a ranar Alhamis.

 

Iftila’in ya faru ne a yankin Kemta Idi-Aba da ke Abeokuta, babban birnin jihar.

Advertisement

 

An Cafke Wani Mutum Da Katin Zabe 29 A Kano

Ya zuwa hada wannan labari ba a samu cikakken bayani ba kan dalilin aukuwar gobarar.

 

Kwamishinan, Dokta Odedina shi ne wanda ya tabbatar da aukuwar gobarar, inda ya ce babu wanda ya rasa ransa a musibar da ta auku.

 

Ya ce yana wajen aiki lokacin da aka kira aka sanar da shi abin da ya faru, wanda kafin isarsa makwabtansa sun taimaka wajen janye motocinsa daga gidan.

Advertisement

 

Daraktan Hukumar Kwana-kwana na Jihar Ogun, ya ce da alama wutar ta samo tushe ne daga dakin girke-girke na gidan.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending