Connect with us

News

Kotu ta hana Shugaba Buhari da Gwamnan CBN kara wa’adin amfani da tsoffin kudi

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

Babbar Kotun Birnin Tarayya ta hana Shugaba Buhari da Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Godwin Emefiele, kara wa’adin amfani da tsoffin takardun Naira da aka sauya fasalinsu.

Advertisement

 

Alkalin kotun, Mai Shari’a Eleoje Enenche ya kuma hana daukacin bankuna da ke Najeriya yin duk wata hulda da ta danganci tsoffin takardun kudin ko neman kara wa’adin amfani da su daga ranar 10 ga watan 10 ga watan Fabrairu da muke ciki.

Advertisement

 

Aƙalla mutum 2,700 aka tabbatar sun rasu a girgizar ƙasar Turkiyya da Syria

Da yake sauraron ƙarar da wasu biyar daga cikin jam’iyyun siyasa 18 da ke Najeriya suka shigar, alkalin ya bukaci shugabannin bankuna da jami’ansu su kawo dalilan da za su hana a kama su da kuma gurfanar da su a gaban kotu kan zargin su da yin zagon kasa ga tattalin arziki, bisa yadda suke boye sabbin takardun Naira 1,000 da N500 da kuma N200 da CBN ya sauya wa fasali ya kuma ba su, amma suke kin ba wa mutane.

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending