Connect with us

News

Matakan da za a bi domin kaɗa ƙuri’a ranar zaɓe – INEC

Published

on

 

 

 

Hukumar Zaɓe mai zaman Kanta a Najeriya INEC ta bayyana matakan da za a bi domin kaɗa ƙuri’a a ranar zaɓe.

 

A wani saƙo da hukumar ta wallafa a shafinta na Tuwita ta bayyana matakai bakwai da ta ce za a bi domin kaɗa ƙuri’a ranar zaɓen.

Advertisement

An kashe mutum ɗaya a yayin faɗa ya ɓarke tsakanin ƴan APC da PDP a Jigawa

A ranar 25 ga watan Fabrairun da muke ciki ne dai za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisun dokokin ƙasar.

 

Matakin farko shi ne lokacin fara zaɓen wanda hukumar ta ce zai fara da misalin ƙarfe 8:30 na safe.

 

Mataki na biyu shi ne gabatar da katin zaɓe ga jami’an zaɓe domin tantance shi ta hanyar amfani da na’urar BVAS.

 

Advertisement

Daga nan sai a duba ko sunan mutum na cikin rajistar masu kaɗa ƙuri’a a wannan rumfar zaɓen.

 

Mataki na gaba shi ne na’urar BVAS za ta tantance mutum ta hanyar saka ɗan yatsarsa a jikinta, daga nan sai a bai wa mutum ƙuri’ar da zai kaɗa.

 

Sai matakin kaɗa ƙuri’a wanda hukumar ta ce ta ware wuri na musamman da za a shiga domin kaɗa ƙuri’ar a asirce.

 

Advertisement

Matakin ƙarshe shi ne bayan kaɗa ƙuri’a mutum zai bar rumfar zaɓen, ko ya yi nesa da rumfar zaɓen na akalla mita 300.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending