Connect with us

News

Matakan da za a bi domin kaɗa ƙuri’a ranar zaɓe – INEC

Published

on

 

 

Advertisement

 

Hukumar Zaɓe mai zaman Kanta a Najeriya INEC ta bayyana matakan da za a bi domin kaɗa ƙuri’a a ranar zaɓe.

Advertisement

 

A wani saƙo da hukumar ta wallafa a shafinta na Tuwita ta bayyana matakai bakwai da ta ce za a bi domin kaɗa ƙuri’a ranar zaɓen.

Advertisement

An kashe mutum ɗaya a yayin faɗa ya ɓarke tsakanin ƴan APC da PDP a Jigawa

A ranar 25 ga watan Fabrairun da muke ciki ne dai za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisun dokokin ƙasar.

 

Advertisement

Matakin farko shi ne lokacin fara zaɓen wanda hukumar ta ce zai fara da misalin ƙarfe 8:30 na safe.

 

Advertisement

Mataki na biyu shi ne gabatar da katin zaɓe ga jami’an zaɓe domin tantance shi ta hanyar amfani da na’urar BVAS.

 

Advertisement

Daga nan sai a duba ko sunan mutum na cikin rajistar masu kaɗa ƙuri’a a wannan rumfar zaɓen.

 

Advertisement

Mataki na gaba shi ne na’urar BVAS za ta tantance mutum ta hanyar saka ɗan yatsarsa a jikinta, daga nan sai a bai wa mutum ƙuri’ar da zai kaɗa.

 

Advertisement

Sai matakin kaɗa ƙuri’a wanda hukumar ta ce ta ware wuri na musamman da za a shiga domin kaɗa ƙuri’ar a asirce.

 

Advertisement

Matakin ƙarshe shi ne bayan kaɗa ƙuri’a mutum zai bar rumfar zaɓen, ko ya yi nesa da rumfar zaɓen na akalla mita 300.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending