News
INEC Ta Fitar Da Jerin Rumfunan Zabe 124 Da Ta Soke
Kwana 10 kafin zaben shugaban kasa, Hukumar Zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta fitar da jerin sunayen rumfunan zabe 124 da ta soke.
INEC ta ce ta soke rumfunan zaben ne a wasu jihohi 15, saboda babu ko mutum daya da ke da rajista a cikinsu, don haka, ba za a yi zabe a nan ba a wannan karon.
2023: Kar ku bari shaidan ya rude ku a yi rigima lokacin zaɓe, Sheikh Nazifi
Jerin sunayen rusassun rumfunan zaben da INEC ta fitar ya nuna Jihar Imo ce a kan gaba da rumfunan zabe 38 da ka soke.
Ga jerin jihohin da abin ya shafa da kuma yawan rumfunan zabensu da INEC ta soke:
Imo – 38
Abia – 12
Borno – 12
Binuwai – 10
Kano – 10
Kaduna – 8
Anambra – 6
Bauchi – 6
Adamawa – 4
Delta – 4
Ebonyi – 4
Enugu – 4
Jigawa – 3
Bayelsa – 2
Edo – 1.
A ranar 25 ga watan Fabrairu da muke ciki ne dai za a gudanar da zaben shugaban kasa na da Majalisun Tarayya, wanda bayansa da mako biyu za a gudanar da na gwamnoni da Majalisun jihohi a ranar 11 ga watan Maris, 2023.
