Connect with us

News

Amurka ta gargaɗi China kan bai wa Rasha tallafi a yakin Ukraine

Published

on

 

 

Advertisement

Sakataren harkokin wajen Amurka, Anthony Blinken ya ce ya gargaɗi China cewa za ta ɗandɗna kuɗarta idan har ta bai wa Rasha wani taimako a yaƙin da take a Ukraine.

 

Advertisement

Mista Blinken ya bayyana haka ne a wata ganawa da babban jami’in diflomasiyyar China, Wang Yi a wani ɓangare na taron tsaro a Munich.

PDP Ta Nemi Buhari da ya tilasta wa ‘yan APC su Saki Sabbin Kudin Da Su Ka Boye

Da yake magana daga bisani, Mista Blinken ya ce Amurka ta samu bayanai cewa China na duba yiwuwar samar wa Rasha makamai abin da ya ce zai janyo babbar matsala ga alaƙarsu.

Advertisement

 

Jami’an biyu sun kuma yi magana kan balan-balan ɗin da aka kakkaɓo daga North Carolina a farkon watan nan.

Advertisement

 

Mista Blinken ya gargaɗi China da kada ta sake ta sake keta sararin samaniyar Amurka yayin da Wang Yi kuma ya ce Amurka ta gurgunta alaƙarsu saboda matakin da ta ɗauka.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending