News
Mun ɗage zaɓen gwamna dana ƴan majalisa ne sabo da mu saita na’urar BVAS
Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, ta ɗage zaben gwamnoni da na ‘yan majalisun jihohi da za a yi ranar 11 ga watan Maris zuwa wata Asabar ɗin, 18 ga Maris.
Ɗage zaɓen ya biyo bayan gazawar hukumar na sake saita na’urar tantance masu kada kuri’a wato BVAS, don zaben jihar.
Kotun Daukaka Kara ta amince da bukatar INEC, Ta yi watsi da Bukatar Obi.
Kotun daukaka kara, a jiya Laraba ta baiwa INEC izinin sake fasalin BVAS din ta, domin zaben gwamnoni da na majalisun Jihohi da za a yi ranar Asabar.
Sai dai kuma INEC ɗin ta ce ba za ta samu damar kammala saita na’urar BVAS ɗin zuwa Asabar ba, shine ta ƙara mako daya domin ta samu damar saita na’urar.
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
