News
Gobara ta tashi a kasuwar Gamboru da ke Maiduguri
Wata gobara ta tashi a kasuwar gamboru da ke tsakiyar birnin Maiduguri a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya.
Rahotonni sun ce gobarar ta ta shi ne da tsakar ranar Asabar lokacin da ake tsaka da kaɗa ƙuri’a a zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisun dokokin jihohi da ake gudanarwa a faɗin ƙasar.
Dole ne a baiwa mata Ilimin Domin Canja Rayuwarsu –Hauwa Wali
Kawo yanzu babu rahotonni rasa rai sakamakon wannan gobara da ta tashi a kasuwar ta kayan abinci a jihar.
Kuma har yanzu ba a kai ga sanin takamaimen abin da ya ya haifar da gobarar ba.
Idan ba a manta ba dai makonni uku da suka gabata wata gobara da ta tashi a kasuwar Monday market a birnin na maiduguri ta yi sanadiyyar asarar miliyoyin dukiyoyi.
A jihar Kano ma an fuskanci gobara a kasuwanni da dama a ƴan kwanakin nan.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
