Connect with us

News

Gobara ta tashi a kasuwar Gamboru da ke Maiduguri

Published

on

 

Wata gobara ta tashi a kasuwar gamboru da ke tsakiyar birnin Maiduguri a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya.

 

Rahotonni sun ce gobarar ta ta shi ne da tsakar ranar Asabar lokacin da ake tsaka da kaɗa ƙuri’a a zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisun dokokin jihohi da ake gudanarwa a faɗin ƙasar.

 

Dole ne a baiwa mata Ilimin Domin Canja Rayuwarsu –Hauwa Wali

Kawo yanzu babu rahotonni rasa rai sakamakon wannan gobara da ta tashi a kasuwar ta kayan abinci a jihar.

Advertisement

 

Kuma har yanzu ba a kai ga sanin takamaimen abin da ya ya haifar da gobarar ba.

 

Idan ba a manta ba dai makonni uku da suka gabata wata gobara da ta tashi a kasuwar Monday market a birnin na maiduguri ta yi sanadiyyar asarar miliyoyin dukiyoyi.

 

A jihar Kano ma an fuskanci gobara a kasuwanni da dama a ƴan kwanakin nan.

Advertisement

 

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending