News
Kakakin majalisar dokokin jihar Yobe ya rasa kujerarsa a hannun Lawan Musa
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Kakakin majalisar dokokin jihar Yobe, Honarabul Ahmed Mirwa Lawan, ya rasa kujerarsa a hannun Lawan Musa mai shekaru 35 dan takarar jam’iyyar PDP a mazabar Nguru II.
Jami’in zaben na jihar, Dakta Habib Muhammad, wanda ya bayyana sakamakon zaben ya ce Musa ya samu kuri’u 6,648 inda ya kayar da kakakin jam’iyyar APC na Yobe wanda ya samu kuri’u 6,466.
NNPP ta bukaci a soke zaben gwamnan Borno
Ya ce sauran ‘yan takarar ADC da NNPP da APM sun samu kuri’u 3,023 da 14 bi da bi.
Daily Trust ta ruwaito cewa Kakakin Majalisar Yobe ya kasance a majalisar tun 2003 lokacin da aka zabe shi a matsayin dan majalisa a karkashin jam’iyyar All Nigeria Peoples Party (ANPP).
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
