Connect with us

News

EFCC Ta Baza Jami’anta guda100 A Kano

Published

on

 

Hukumar Yaki da Yi wa Tattalin Arzikin Kasa Zagon Kasa (EFCC), ta tura jami’anta 100 don yaki da sayen kuri’u a Kano, Katsina da kuma Jigawa a yayin karasa zaben da za a yi ranar Asabar a jihohin.

Advertisement

 

Kwamandan EFCC na shiyyar Kano, Farouk Dogondaji ne, ya bayyana hakan a wata hira da ya yi da Kamfanin Dillancin Labarai (NAN) a Kano a ranar Juma’a.

Advertisement

 

Daliban Jami’ar Gusau Da Aka Yi Garkuwa Da Su Sun Kubuta

“Mun tura jami’ai 20 domin sanya ido kan yadda zaben ‘yan majalisar jiha zai gudana a Kafur da Kankara a Jihar Katsina,” in ji shi.

Advertisement

 

Ya kuma bayyana cewa an kuma tura isassun ma’aikata domin sanya ido a mazabar Tudun Wada da Doguwa da Takai da kuma wasu mazabu na ‘yan majalisar jiha a Jihar Kano.

Advertisement

 

 

Advertisement

Dogondaji, ya ce an kuma tura wasu ma’aikata domin sa ido kan zabukan ‘yan majalisar dokoki a Katsina da Jigawa domin hana sayen kuri’u.

 

Advertisement

“Mun kuma tura jami’ai zuwa filin jirgin sama na Malam Aminu Kano da ke Kano domin sanya ido game da wadanda za su shigo jihar.

 

Advertisement

“Zamu fito fili a dukkan rumfunan zabe a Kano, Katsina da Jigawa domin sanya ido kan yadda za a gudanar da zabe da kuma bayan zabe.

 

Advertisement

 

“Za mu kasance a wurare tattara sakamakon zabe a kananan hukumomin da za a karasa zaben.

Advertisement

 

 

Advertisement

“Za mu yi hadin gwiwa tare da jami’an tsaro na jihar don samar da yanayi na lumana ga masu zabe,” in ji shi.

 

Advertisement

Ya ce tura jami’an na daga cikin kudirin hukumar na tabbatar da sahihin zabe a yankunan da za a karasa zaben.

 

Advertisement

Kwamandan, ya ce EFCC ta kuma dauki matakai, wadanda za su yi wahala ga wani mutum ko kungiya wajen yin magudi a zaben.

 

Advertisement

Dogondaji, ya yi kira ga ma’aikatan hukumar da su kasance masu kwazo da kwarewa wajen gudanar da aikinsu.”

 

Advertisement

 

Ya shawarci iyaye kan kada su bari a yi amfani da ’ya’yansu wajen aikata bangar siyasa, wanda a cewarsa duk wanda aka kama za a gurfanar da shi a gaban kuliya.

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending