Connect with us

News

INEC ta bai wa Ado Doguwa shaidar cin zaɓen ɗan majalisa

Published

on

Hukumar zaɓe ta Najeriya ta bai wa Alhassan Ado Doguwa shaidar sake cin zaɓe a matsayin ɗan majalisar wakilai daga mazaɓar Doguwa da Tudun Wada.

Karo na biyar kenan, da ɗan majalisar na tarayya ke samun nasarar zuwa majalisar wakilai daga Kano tun bayan dawowar Najeriya mulkin dimokraɗiyya a 1999.

Advertisement

INEC za ta bai wa Fintiri shaidar cin zaɓensa yau La

Tun da farko dai an soke nasarar da ya samu, bayan zaɓen 25 ga watan Fabrairu, saboda jami’in sanar da sakamako, Farfesa Ibrahim Adamu Yakasai ya ce “tursasa masa” aka yi.

Sai dai, jami’in sanar da sakamako a zaɓen cike-giɓi na mazaɓar, Farfesa Sani Ibrahim a ranar 15 ga watan Afrilu, ya ayyana Alhassan Doguwa a matsayin wanda ya yi nasara bayan wannan zaɓe.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending