News
Hukumar NDLEA Ta Kama Mutum 26 Kan Zargin Safarar Kwayoyi A Gombe
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Hukumar Hana sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta kama wasu mutum 26 da ake zargin da safarar kwayoyi a Jihar Gombe.
Hukumar ta kuma ce ta sami nasarar kama kwaya mai nauyin kilogram 2.654.
Jami’in hulda da Jama’a na hukumar a jihar, Henry E. Ihebuzor, ne ya sanar da hakan a wata takarda da ya raba wa manema labarai a Gombe.
Ya ce hukumar ta samu nasarar ce a wani samame na musamman da ta gudanar bisa umurnin Shugaban hukumar na kasa Birgediya Janar Buba Marwa mai ritaya
Ya love kwayoyin da aka kama sun hada da Tabar Wiwi mai nauyin kilogiram 2.570 da kuma wasu kwayoyin masu nauyin kilogiram 84.
Hukumar ta gargadi dilolin kwaya da masu sayarwa a jihar da su guji wannan sana’a don gudun fuskantar fushin hukuma, inda yace idanun su na kowanne lungu da sako dan magance harkar miyagun kwayoyin.
-
News16 hours ago
Jam’iyyar Labour Party Ta Yi Alkawarin Kafa Hukumar Kula Da Hayar Gidaje A Kano
-
News3 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News6 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
