News
Gwamnatin Jihar Kano Zata Saka Gina Ginin Da Ta Rushe Na Shataletalen Gidan Gwamna
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Gwamnatin Jihar Kano tace zata sake gina ginin da ta rushe a shataletalen gidan gwamnati.
Gwamnan Kano Engr Abba Kabir Yusuf ne ya bayyana hakan bayan da ya gana da wadda ta kirkiro taswirar zanen zanen ginin.
Matsan garin Geidam Masu amfani Facebook zasu gudanar da gagarin taron sada zumunta karo na farko.
Cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labarai gwamnan Hisham Habib ya fitar, ya ce a yanzu gwamnatin zata yi sabon ginin a Fly Over ta Naibawa.
Gwamnan Abba Kabir yace bayan sun yi bincike, sun gano cewa wurin da za’a sake ginin nan ne ya fi dacewa, inda bazai yi barazanar ga masu wucewa da ababan hawa ba.
Wadda ta zana ginin Kaltume Gana ta gode wa gwamnan akan wannan ƙudurin nasa, kasancewar bai bari tayi wahala a banza ba.
An dai zana ginin domin murnar cikar Kano shekara 50 da kafuwa.i
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
