Connect with us

Politics

Ba ka isa ka karɓe mana gurbin muƙamin minista ba, APC ta faɗawa Wike

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Jam’iyyar APC, reshen jihar Rivers, ta karyata rade-radin da wasu ke yi na cewa ta mika wa tsohon Gwamna Nyesom Wike gurbin mukamin minista daga jihar.

APC ta ce ta yi mamakin gani a wasu jaridun kasar nan cewa jam’iyyar ta mika wa wanda ba dan jam’iyyar APC ba a jihar Rivers gurbin mukamin minista.

Kungiyar ‘yan jaridu ta yanar gizo ta Kano ta yi murnar nada babban mambansu Hisham Habib a matsayin Manajan Daraktan gidan rediyon Kano.

Ta yi nuni da cewa jam’iyyar reshen jihar ba ta taba ganawa da ƙungiyar Amalgamated Bola Tinubu Campaign Council domin tana da kungiyoyi masu zaman kansu da kungiyoyin tallafi sama da dari wadanda suka yi wa jam’iyyar APC aiki a jihar Rivers.

“Babu wata kungiya mai zaman kanta ko wani mutum da ba a tsarin jam’iyyar da aka amince da shi a hukumance da ke da ikon bai wa tsohon gwamnan jihar duk wani hakki na jam’iyya ba, kuma tabbas kowa ya san cewa shi ɗan jam’iyyar PDP ne mai ɗauke da katin jam’iyyar.

Advertisement

Da ya ke jawabi ga manema labarai a Fatakwal, a jiya Laraba, Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Darlington Nwauju, ya ce, “Muna mamakin daga ina kungiya ko wani mutum ya samu ikon yin magana da yawun APC. Sai dai a karo na goma sha uku muna so mu ce Mista Tony Okocha ba dan babbar jam’iyyarmu ba ne, kuma ba mu samu wata sanarwa daga sakatariyar jam’iyyar mu ta kasa ba cewa an ba shi izinin shiga jam’iyyar mu.

“Muna son murkushe wannan jita-jita a hukumance da aka yi niyya don tattara burin siyasar tsohon Gwamna Wike. Don haka mun yi watsi da wannan izgili da cin zarafi da ake yi wa hankalinmu a matsayinmu na jam’iyyar siyasa ba.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending