Politics
Ba ka isa ka karɓe mana gurbin muƙamin minista ba, APC ta faɗawa Wike
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Jam’iyyar APC, reshen jihar Rivers, ta karyata rade-radin da wasu ke yi na cewa ta mika wa tsohon Gwamna Nyesom Wike gurbin mukamin minista daga jihar.
APC ta ce ta yi mamakin gani a wasu jaridun kasar nan cewa jam’iyyar ta mika wa wanda ba dan jam’iyyar APC ba a jihar Rivers gurbin mukamin minista.
Ta yi nuni da cewa jam’iyyar reshen jihar ba ta taba ganawa da ƙungiyar Amalgamated Bola Tinubu Campaign Council domin tana da kungiyoyi masu zaman kansu da kungiyoyin tallafi sama da dari wadanda suka yi wa jam’iyyar APC aiki a jihar Rivers.
“Babu wata kungiya mai zaman kanta ko wani mutum da ba a tsarin jam’iyyar da aka amince da shi a hukumance da ke da ikon bai wa tsohon gwamnan jihar duk wani hakki na jam’iyya ba, kuma tabbas kowa ya san cewa shi ɗan jam’iyyar PDP ne mai ɗauke da katin jam’iyyar.
Da ya ke jawabi ga manema labarai a Fatakwal, a jiya Laraba, Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Darlington Nwauju, ya ce, “Muna mamakin daga ina kungiya ko wani mutum ya samu ikon yin magana da yawun APC. Sai dai a karo na goma sha uku muna so mu ce Mista Tony Okocha ba dan babbar jam’iyyarmu ba ne, kuma ba mu samu wata sanarwa daga sakatariyar jam’iyyar mu ta kasa ba cewa an ba shi izinin shiga jam’iyyar mu.
“Muna son murkushe wannan jita-jita a hukumance da aka yi niyya don tattara burin siyasar tsohon Gwamna Wike. Don haka mun yi watsi da wannan izgili da cin zarafi da ake yi wa hankalinmu a matsayinmu na jam’iyyar siyasa ba.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
