News
Dole Mu Kalubalanci Duk Wani Yunkuri Na Kuntatawa ‘Yan Najeriya – NLC,
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Kungiyar kwadago ta kasa NLC ta yi barazanar daukar mataki a hannunta biyo bayan karin farashin man fetur.
Kungiyar ta NLC a cikin wata sanarwa da ta fitar ta hannun shugabanta na kasa Joe Ajaero, ta zargi gwamnatin Tinubu da tatse talakawa domin hidimtawa masu hannu da shuni da kuma jefa ‘yan Najeriya cikin wahala.
Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Nazari Kan Tallafin Naira Dubu 8 Ga Gidajen Talakawa Masu Rauni
Ya kuma yi nuni da kudirin biyan ‘yan majalisar dokokin kasarnan zunzurutun kudi har naira biliyan 70 da Naira billiyan 36 ga bangaren Shari’a yana maibayyana hakan amatsayin mafi girman karkatar da kudade cikin aljihun jami’an gwamnati.
Ita kuwa, kungiyar kwadago ta TUC ta bakin mataimakin shugabanta na kasa, Tommy Etim, ita ma ta caccaki gwamnatin tarayya kan karin farashin man fetur, inda ta ce yanzu kasarnan na fuskantar rudanin tattalin arziki.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
