News
Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Nazari Kan Tallafin Naira Dubu 8 Ga Gidajen Talakawa Masu Rauni
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bada umarnin a sake fasalta shirin bada kudi Naira dubu 8 da aka tsara domin tallafi ga gidajen Talakawa da sukafi rauni a Najeriya.
Mai magana da yawun shugaban kasar, Dele Alake, a wata sanarwa da ya fitar, ya ce umarnin ya biyo bayan sauraron ra’ayoyin da ‘yan Najeriya suka bayyana akan tsarin.
Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Daukar Hayar Kungiya Domin Bata Sunan Tsohuwar Gwamnati
Alake ya ce shugaban kasar ya kuma bayar da umarnin a gabatarwa ‘yan Najeriya gaba daya tsarin tallafin da gwamnati zata bayar domin ba iya shirin tallafin kudi ba ne kadai a jimillah tsare-tsaren Rage radadin.
Alake ya ce shugaba Tinubu amatsayin jagora mai sauraron Jama’arsa ya kuma ba da umarnin a gaggauta sakin takin zamani da hatsi ga manoma da gidaje miliyan 50 a fadin jihohi 36 da kuma babban birnin tarayya Abuja.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
