Connect with us

News

Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Nazari Kan Tallafin Naira Dubu 8 Ga Gidajen Talakawa Masu Rauni

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bada umarnin a sake fasalta shirin bada kudi Naira dubu 8 da aka tsara domin  tallafi ga gidajen Talakawa da sukafi rauni a Najeriya.

Mai magana da yawun shugaban kasar, Dele Alake, a wata sanarwa da ya fitar, ya ce umarnin ya biyo bayan sauraron ra’ayoyin da ‘yan Najeriya suka bayyana akan tsarin.

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Daukar Hayar Kungiya Domin Bata Sunan Tsohuwar Gwamnati

Alake ya ce shugaban kasar ya kuma bayar da umarnin a gabatarwa ‘yan Najeriya gaba daya tsarin tallafin da gwamnati zata bayar domin ba iya shirin tallafin kudi ba ne kadai a jimillah tsare-tsaren Rage radadin.

Alake ya ce shugaba Tinubu amatsayin jagora mai sauraron Jama’arsa ya kuma ba da umarnin a gaggauta sakin takin zamani da hatsi ga manoma da gidaje miliyan 50 a fadin jihohi 36 da kuma babban birnin tarayya Abuja.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending