News
Rundunar Sojin Ruwa Sun Dakile Yunkurin Balle Rumbun Ajiyar Abinci A Kano
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.
Rundunar sojin ruwa ta kasa tace tayi nasarar dakile yunkuri fasa rumbunan ajiyar kayan abinci ajihar Kano a ranar da kungiyoyin kwadago suka gudanar da zanga-zangar adawa da tsadar Rayuwa.
Shugaban kwalejin horas da jami’an sojojin ruwa dake Dawakin Tofa, Usman M Bugaji ne ya bayana hakan yayin faretin bankwana bayan ya shafe kusan shekara biyu a matsayin kwamandan kwalejin.
Kasar Senegal tace a shirye take ta dauki matakin soja kan Jamhuriyar Nijar
Bugaji yace an samu nasarar hana wasu matasa balle rumbun ajiyar abinci dake kasuwar Dawanau a cikin dare yayin zanga-zangar kungiyoyin kwadago.
Haka kuma yace rundunar tayi nasarar dakile wani yunkurin yin safarar wasu mata guda 18 daga jahar Kano zuwa kasar Libya.
Arewa radio ta rawaito cewa sabon kwamandan kwalejin Comodore James Kolade Adedeji, ya ce zai cigaba da bunkasa alakar dake tsakanin kwalejin da kuma al’ummar yankin domin samar da ingantaccen tsaro.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
