News
Yan sanda sun tabbatar da sace basaraken gargajiya da matarsa a Nasarawa
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.
Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta tabbatar da sace Sarkin Gurku, Jibrin Mohammed da matarsa da wasu ‘yan bindiga suka yi a garin Gurku da ke karamar hukumar Karu a jihar.
DSP Ramhan Nansel, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan ne ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin a ranar Litinin, inda ya kara da cewa an yi garkuwa da sarkin ne a fadarsa.
A cewar Nansel, a ranar 6 ga watan Agusta, rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta samu kiran waya cewa wasu mutane da ake zargin masu garkuwa da mutane ne suka mamaye fadar garin Gurku mai tazarar kilomita 10 daga babban garin Mararaba a karamar hukumar Karu.
Ya kara da cewa bayan samun labarin, kwamishinan ‘yan sandan jihar Nasarawa, CP Maiyaki Mohammed-Baba, ya tura tawagar jami’an ‘yan sanda tare da hadin gwiwar ’yan banga zuwa wurin.
“Da isowarsu, an gano cewa an yi garkuwa da basaraken da matarsa zuwa inda ba a sani ba.
Sai dai ya bayar da tabbacin cewa kwamishinan ya kara tura karin wasu mutane daga cikin tawagar kwararru da kuma masu yaki da masu garkuwa da mutane da kuma mutanen da suka fito daga yankin Karu zuwa wurin.
“Ana ci gaba da kokarin ceto basaraken da matarsa ba tare da samun rauni ba. Za a sanar da jama’a yayin da al’amura ke faruwa,” inji shi.
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
