Connect with us

News

Kotu Ta Kwace Kujerar Dan Majalisar Tarayya Na Tarauni na NNPP ta Baiwa APC

Published

on

Spread the love

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.

Kotun sauraren kararrakin zabe ta jihar Kano Dake a Miller road ta kwace Kujerar Dan majalisar tarayya na karamar hukumar Tarauni Hon Muktari Yarima na NNPP ta dawo da ita hannun Hon Hafizu Kawu na Jami’iyar APC.

Kotun mai alkalai uku, ta tabbatar da Hon Hafiz Ibrahim Kawu na Jam’iyyar APC amatsayin wanda ta mikawa kujerar bisa dogaro da hujjar gabatar da sakamakon bogi na Firamare da Danmajalisar Yarima yayi.

Advertisement

An Saka Dokar Hana Fita A Jihar Gombe.

Yarima dai ya tsaya ne karkashin inuwar Jam’iyyar NNPP a zaben da akayi a watan Fabarerun daya gabata.
Jim kadan bayan fitowa daga kotun, lauyan Mukhtar Yarima Barista Rabiu Sadiq yace sun karbi wannan hukunci kuma zasu daukaka kara

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *