News
Gwamnatin Jahar Kano Ta Soke Lasisin Makarantu Masu Zaman Kansu
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.
Gwamnatin jihar Kano ta soke takardar shaidar aiki na dukkan makarantu masu zaman kansu da ke aiki a fadin jihar.
An dauki matakin ne a ranar Asabar a yayin wani taro da masu makarantu masu zaman kansu dake jihar.
Zanga-Zanga Ta Barke A Kano Kan Yunkurin Daukar Matakin Soji A Jamhuriyyar Nijar.
Mai baiwa gwamna shawara na musamman kan cibiyoyin masu zaman kansu da na sa kai, Alhaji Baba Umar ya bayyana cewa ana bukatar dukkan makarantu masu zaman kansu da su gaggauta kammala yin sabbin rajistar fom, saboda gwamnati ta kaddamar da shirin bayar da sabbin ta kardun shaida.
Umar ya bayyana cewa matakin ya jaddada kudirin gwamnati na ganin cewa makarantu masu zaman kansu sun bi ka’idojin da aka gindaya na aiki a jihar.
“An tunatar da masu makarantu masu zaman kansu alhakin da ya rataya a wuyansu na biyan harajin kashi 10 ga gwamnati. Wannan
