Connect with us

News

Majalisa za ta binciki ayyuka 10,000 da aka yi watsi da su

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Mataimakin shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawan Najeriya, Sanata Kamorudeen Lere Oyewumi ya bayyana cewa kawo yanzu majalisar ta gano ayyukan gwamnati sama da 10,000 da aka yi watsi da su a matakai daban-daban a fadin kasar.

Advertisement

Oyewumi ya ce, Majalisar Dokoki ta Tarayya ta amince da gudanar da cikakken bincike kan ayyukan da aka yi watsi da su da nufin farfado da su a inda ya dace domin ci gaban al’umma.

Gwamanan Kano Ya Sake Nada Nasiru Kassim Fulatan Babban Mai Taimakawa kan Makaranatun Kimiyya da Fasaha da Kuma wasu 56

Sanatan mai wakiltar Osun ta Yamma a lokacin da yake zantawa da manema labarai, ya bayyana cewa an gudanar da binciken ne domin gano ci gaban ayyukan da dalilan watsi da su.

Advertisement

Ya ce an tattaro kwararru a fannoni daban-daban domin tantance fa’ida da kuma nawa ne gwamnati mai ci za ta kashe wajen farfado da ayyuka.

Tsohon kwamishinan hukumar kula da ƙidayar jama’a ta NPC, ya kara da cewa ’yan kwangilar da suka yi watsi da ayyukan za a gano su tare da karfafa musu gwiwa su koma wuraren aiki.

Advertisement

Ya kara da cewa duk inda aka samu wanda ya saba wa doka, to za a mika irin wannan mutumin ga hukumomin yaki da cin hanci da rashawa domin daukar matakin da ya dace.

Sanatan, wanda ya koka da yadda batun watsi da ayyukan ya zama abin damuwa kuma ba za a iya jurewa ba, ya bayyana cewa gwamnati mai ci za ta dauki tsauraran matakai don rage mummunan abin kunya na kasa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending