Connect with us

News

Gwamnatin jihar Kano ta ce sama da yara 520 ne ake fargabar sun mutu sakamakon bullar cutar mashako

Published

on

Gwamnan jahar Kano Abba Kabir Yusuf

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA

 

Advertisement

Gwamnatin jihar Kano ta ce sama da yara 520 ne ake fargabar sun mutu sakamakon bullar cutar mashako a jihar.

Darakta Janar na Hukumar Kula da Lafiya a matakin farko ta Jihar Kano Dakta Muhammed Nasir Mahmoud ne ya tabbatar da hakan a lokacin da yake magana a taron wayar da kan ‘yan jarida na kwana daya kan bullar cutar mashako a jahar Kano wanda aka gudanar ranar Talata.

Advertisement

Yakin Da Ake Yi A Sudan Ya Fantsama Zuwa Yankin Port Sudan

Ya ce tun bayan bullar cutar a watan Disambar 2022 jihar Kano ta samu mutane 8700 da ake zargin sun kamu da cutar inda 6300 aka tabbatar sun kamu da cutar.

 

Advertisement

Ya ce daga cikin kananan hukumomi 44 na jihar Kano, cutar mashako ta yadu zuwa kananan hukumomi 39 da cutar ta fi kamari inda ba a yi allurar rigakafin cutar ba.

A cewarsa, kashi 27% ne kawai aka yiwa allurar riga-kafin, kashi 7.5% an yiwa kashi 59.9% kuma kashi 5.5

Advertisement

Ya ce gwamnatin jihar Kano tare da goyon bayan gwamnatin tarayya suna aiki kafada da kafada domin kawo karshen cutar nan da Disamba, 2023.

 

Advertisement

Manajan kula da lafiya na UNICEF Dr. Serekeberehan S. Deres ya ce halin da yaran da ba a yi musu alluran rigakafi ba na da matukar muhimmanci, ba za a amince da su ba, kuma suna bukatar a gaggauta magance.

 

Advertisement

A cewar NCDC “Bayanan sun nuna, kashi 60.7 cikin 100 na wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar mashako ba su da kashi daya, ma’ana ba a yi musu allurar kwata-kwata ba.”

 

Advertisement

Ya ce wasu daga cikin alamomin cutar sun hada da, ciwon makogwaro, wahalar numfashi ko saurin numfashi, zazzabi da sanyi.

Ya yi nuni da cewa, Najeriya na bukatar karfafa aikin rigakafi na yau da kullun zuwa dan magance wannan kalubale.

Advertisement

Don haka Dr Deres ya yi kira ga mahalarta taron da su kasance masu taka-tsan-tsan wajen wayar da kan masu hannu da shuni, da gwamnati, da iyalai, da al’umma, da kowa da kowa, kan mahimmancin rigakafin yau da kullum.

An bayyana cewa kashi 80 cikin 100 na masu cutar mashako an samu su a jihar Kano kuma 60.8

Advertisement

daga ciki yara ne.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending