News
Kotu ta tabbatar da Nasiru Gawuna a matsayin gwamnan Kano
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Kotun sauraren kararrakin zaben gwamnan jihar kano ta tabbatar da Dr. Nasiru Yusuf Gawuna na jam’iyyar APC a matsayin halastaccen gwamnan jihar kano.
Kotun Mai alkalai guda karkashin jagorancin mai shari’a Oluyemi Akintan Osadebay ce ta tabbatar da hakan yayin zaman sama da awanni 8 ta na’urar zoom.
Akwai Yiwuwar Ta Yanar Gizo Za A Yanke Hukuncin Zaben Gwamnan Kano
Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito bayan da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta bayyana Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP a matsayin gwamnan jihar kano, hakan tasa jam’iyyar APC ta garzaya gaban kotu don ƙalubalantar nasarar da Abba Kabir ya Samu.
Yayin zaben dai INEC ta ce Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP ya samu kuri’u Sama da Miliyan 1 yayin da ta ce Dr. Nasiru Yusuf Gawuna na jam’iyyar APC ya Sami kuri’u Sama da Dubu dari takwas.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
