Connect with us

News

Tallafin rage raɗaɗi: Kungiyar SERAP ta maka gwamnoni a kotu kan tallafin N72bn

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

Ƙungiyar nan mai rajin a yi aiki da gaskiya da aka fi sani da SERAP a taƙaice, na zargin gwamnonin jihohi 36 kan rashin bada cikakken bayani game da yadda suka sarrafa Naira biliyan 72 da aka ba su a matsayin tallafin rage raɗaɗin cire tallafn fetur da gwamnati ta yi.

Cikin sanarwar da ta fitar a ranar Lahadi ta bakin Daraktanta, Kolawole Oluwadare, ƙungiyar ta ce ta shigar da ƙara a kan gwamnonin, tare da neman cikakken bayani daga gare su game da waɗanda aka tsara su ci gajiyar shirin da kuma kayayyakin da suka saya da kuɗin da aka ba su.

Advertisement

Jawabin Da Shugaba Tinubu Da Yayi Na Ranar Independence Bashida Wata Ma’ana -PDP

A baya-bayan nan Gwamnatin Tarayya ta raba wa jihohin kuɗi Naira biliyan bibbiyu a matsayin ɓangare na biliyan biyar-biyar da ta ware wa kowace jiha don rage raɗaɗin cire tallafin fetur.

Ƙarar mai lamba FHC/L/CS/1943/2023 wadda aka shigar a Juma’ar da ta gabata a Babbar Kotun Tarayya da ke Legas, SERAP ta nemi kotu ta bai wa gwamnonin jihohin ƙasar nan 36 umarnin kowannensu ya fito ya yi bayanin yadda ya kashe biliyan biyun da aka ba shi don amfanin talakawansa.

Advertisement

Kazalika, ƙungiyar ta nemi kotu da ta bai wa gwamnonin umarni a kan su bai wa ICPC da EFCC odar su sanya ido kan yadda suka kashe kuɗaɗen tallafin da aka ba su, da dai sauransu.

Kawo yanzu dai ba a tsayar da ranar da kotun za ta fara sauraren ƙarar ba.

Advertisement

Rahotanni daga sassan ƙasa sun nuna yadda jama’a suka yi ta ƙorafi game da kayan abincin da gwamnatocin jihohi suka raba musu da sunan tallafin rage raɗaɗin cire tallafin fetur.

Wani labarin kuma Jawabin Da Shugaba Tinubu Da Yayi Na Ranar Independence Bashida Wata Ma’ana -PDP

Advertisement

 

A yayin da ake cigaba da samun cikas wajen balaguro a filin jirgin sama na Murtala Muhammed dake Legas, biyo bayan komawar da kamfanonin jiragen sama na kasashen waje suka yi zuwa sabuwar tashar jiragen sama, gwamnatin tarayya ta gayyaci kamfanonin jiragen sama na kasashen waje zuwa wani taro a yau.

Advertisement

 

A sakamakon haka, kwamitin da ministan harkokin sufurin jiragen sama, Festus Keyamo ya kafa domin duba rudanin tafiye-tafiye a filin jirgin sama naMurtala Muhammad da kwamitin ministoci zai gana da masu ruwa da tsaki a domin nemo bakin zaren da warware matsalar.

Advertisement

 

Fasinjojin kasa da kasa da suka tashi daga Najeriya a ranakun Laraba da Alhamis sun makale a biranen Legas da Cairo da Doha da Landan, da sauran wurare bayan da madaurin kaya na jirgi ya lalace a sabon filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Legas, al’amarin da ya tilastawa kamfanonin jiragen sama jinkirtawa tare da soke tashin jirage.

Advertisement

 

Har yanzu zuwa karshen mako matsalar tafiye-tafiye na ci gaba da wanzuwa inda fasinjojin ke kwashe sa’o’i a kan layi domin tantance su ta hanyar binciken tsaro

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending