Connect with us

News

Gwamnan Jahar Nasarawa Ya Lashi Takobin Ɗaukaka Kara Kan Soke Zabensa

Published

on

Spread the love

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Jagoran Alkalan Kotun sauraron kararrakin zaben Gwamnan Jihar Nasarawa, Justice Ezikel Ajayi, ya bayyana cewa, bayanan da na’urar zabe ta BVAS da IREV suka bayar ya bambamta da Wanda aka rubuta a takarda.

Advertisement

Alkalin ya soke zunzurutun kuri’un da aka bewa dan takarar Gwamna a jam’iyyar APC wadanda ba suyi dai-dai da na BVAS ba.

QWasu Ƴan Bindiga Sun Yi Ɓarin Wuta A Funtua

Sabida haka ne, mai shari’ar ya kwace sakamakon da ya ayyana jam’iyyar APC a matsayin wadda ta lashe zaben kujerar gwamnan ta mayar wa Jam’iyyar PDP.

Alkalan Kotun guda biyu sun dogarane da wannan hujar inda sukace Gwamna Abdullahi Sule na Jam’iyyar APC bai kai ga nasara ba. Don haka kotu ta tabbatar da nasarar mai kara Hon. David Emmanuel Ombugadu na Jam’iyyar PDP a matsayin Wanda ya lashe zaben Gwamnan Jihar Nasarawa.

Advertisement

Da yake zantawa da manema Labarai a gidan Gwamnati jim kadan bayan zartar da hukuncin kotun, Gwamna Abdullahi Sule ya ce, “Duk da hukuncin da Kotun sauraron kararrakin zaben ta yanke, har yanzun ni ne Gwamnan Jihar Nasarawa, Kuma zan daukaka kara zuwa kotun gaba.

“Ina kira agareku magoya bayana da kuyi hakuri da abinda kuka ji. Ina nan a matsayin Gwamna, zamu daukaka kara. Wannan hukunci ne na kotun sauraron kararrakin zabe ba na Kotun koli ba.

“Kuma zan ci gaba da yin ayyukan ci gaban kasa kamar yadda muke yi. Duk abinda za a fada muku, kar ya bakanta muku rai. Allah yakan jarrabi Bawa ta yadda yaso.”

Advertisement

Wani labarin kuma Wasu Ƴan Bindiga Sun Yi Ɓarin Wuta A Funtua

 

A yayin da ake cigaba da samun cikas wajen balaguro a filin jirgin sama na Murtala Muhammed dake Legas, biyo bayan komawar da kamfanonin jiragen sama na kasashen waje suka yi zuwa sabuwar tashar jiragen sama, gwamnatin tarayya ta gayyaci kamfanonin jiragen sama na kasashen waje zuwa wani taro a yau.

Advertisement

 

A sakamakon haka, kwamitin da ministan harkokin sufurin jiragen sama, Festus Keyamo ya kafa domin duba rudanin tafiye-tafiye a filin jirgin sama naMurtala Muhammad da kwamitin ministoci zai gana da masu ruwa da tsaki a domin nemo bakin zaren da warware matsalar.

 

Advertisement

Fasinjojin kasa da kasa da suka tashi daga Najeriya a ranakun Laraba da Alhamis sun makale a biranen Legas da Cairo da Doha da Landan, da sauran wurare bayan da madaurin kaya na jirgi ya lalace a sabon filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Legas, al’amarin da ya tilastawa kamfanonin jiragen sama jinkirtawa tare da soke tashin jirage.

 

Har yanzu zuwa karshen mako matsalar tafiye-tafiye na ci gaba da wanzuwa inda fasinjojin ke kwashe sa’o’i a kan layi domin tantance su ta hanyar binciken tsaro

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *