Politics
Dino Melaye Ya Bukaci INEC Ta Soke Zaben Kananan Hukumomi Biyar
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Dino Melaye, dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a jihar Kogi, ya bukaci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ta soke zaben kananan hukumomi biyar na jihar saboda abinda ya kira runton kuri’u da kuma sayen masu zabe da kudi.
Melaye ya bayyana kananan hukumomin da abin ya shafa da su ne Okene, Okehi, Ajaokuta, Adavi, da Ogori/Mangogo, yana mai cewa an tabka magudi a sakamakon zaben.
Dole ne INEC ta soke zaben a kananan hukumomi 5 na Kogi-Tsakiya. Zaben da aka yi a Okene, Okehi, Ajaokuta, Adavi, da Ogori/Mangogo wata zamba ce da aka hada kai daga babban mataki na INEC Melaye ya wallafa a shafinsa na X.
Tun da farko, wata kungiyar farar hula mai suna YIAGA Africa, ta yi tsokaci kan gano sakamakon zabe daga sashin zabe na 004 da ke Eni Ward na yankin Ogori/Mangogo.
An ga sakamakon jabun yayin da masu kada kuri’a ke cikin jerin gwano,sai kuma ga sakamakon mazabar a hannun wasu suna yayatawa a kafafen sadarwa.
A sakamakon zaben, wanda aka makala kwafinsa a kan yanar gizo ya nuna cewar Jam’iyar APC ta samu kuri’u 200; AA ta ci 1; yayin da ADC, PDP da SDP suka samu kuri’u 2 kowanne.
A wani labarin kuma KNSG ta shirya taron karawa juna sani na kwanaki biyu na masu ruwa da tsaki KSCHMA DRF, na asibitoci.
Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.
Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.
A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.
Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.
