Connect with us

News

Za A Binne Gawarwaki 60 Da Ba A Gano ’Yan Uwansu Ba A Jihar Kaduna

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

Gwamnatin Jihar Kaduna za ta binne gawarwakin wasu mutane 60 da ba a san masu su ba.

Sashin Lafiya na Karamar Hukumar Kaduna ta Kudu zai dauki gawawwakin don binnewa a a Makabartar Layin Bashama da ke unguwar Tudun Wada.

NNPP Ta Baiyana Bukatar Atiku Na Yin Sabuwar Maja A Matsayin Shan Magani Bayan Mutuwa

Mataimakiyar Sashin lafiya na Karamar Hukumar Kaduna ta kudu- Asmau Saidu Adamu ta sanar cewa za a binne gawarwakin ne a ranar Juma’a 17 ga watan Nuwamba da muke ciki.

“Za a dauko gawarwakin ne daga Asibitin Gwamna Awan zuwa Makabartar Bashama Road, karkashin jagorancin Kwamishinar Lafiya ta Jihar Kaduna, Umma K Ahmed da Shugaban Asibitin Gwamna Awan, Dokta Gebriel Brown,” inji ta.

Advertisement

A wani labarin kuma NNPP Ta Baiyana Bukatar Atiku Na Yin Sabuwar Maja A Matsayin Shan Magani Bayan Mutuwa

Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.

Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.

A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.

Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending