News
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Rasa Raukan Mutane 50 a Somaliya

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Ambaliyar ruwa a Somaliya ta Yi Sanadiyyar Rasa Rayukan mutane 50 tare da korar kusan 700,000 daga gidajensu, in ji wani jami’in gwamnati, inda ake sa ran ruwan sama mai karfi da ya fara a ranar Talata zai kara dagula halin da kasar ke ciki.
Yankin na kahon Afirka na fama da ruwan sama kamar da bakin kwarya da ambaliyar da ke da nasaba da yanayin El Nino, lamarin da ya yi sanadin asarar rayuka da dama tare da haddasa rarrabuwar kawuna, ciki har da Somaliya, inda ruwan sama ya lalata gadoji tare da mamaye wuraren zama.
“Mutane 50 ne suka Rasa Rayukan su a cikin bala’in, yayin da aka tilastawa mutane 687,235 barin gidajensu,” in ji darektan hukumar kula da bala’o’i ta Somalia, Mohamud Moalim Abdullahi a wani taron manema labarai a ranar Litinin ya bayyana.
Ya kara da cewa “Yawan Ruwan da ake sa ran za a yi tsakanin ranakun 21 zuwa 24 ga watan Nuwamba zai karu.
A ranar Asabar, hukumar jin kai ta Majalisar Dinkin Duniya OCHA ta ce adadin mutanen da ruwan ya raba da muhallansu sakamakon ruwan sama mai karfi da ambaliyar ruwa a Somaliya “ya kusan ninki biyu cikin mako guda”, yayin da mutane miliyan 1.7 ke fama da bala’in gaba daya.
“Bugu da kari, tituna, gadoji da filayen jiragen sama sun lalace a yankuna da dama, lamarin da ya shafi zirga-zirgar jama’a da kayayyaki tare da haifar da karin farashin kayayyakin masarufi,” in ji OCHA.
Kungiyar agaji ta Save the Children ta Burtaniya a ranar Alhamis ta ce sama da mutane 100 da suka hada da kananan yara 16 ne suka Rasa Rayukan su yayin da aka tilastawa wasu sama da 700,000 barin gidajensu a kasashen Kenya da Somaliya da Habasha sakamakon ambaliyar ruwa.
Yankin yana fama da fari mafi muni a cikin shekaru arba’in bayan rashin damina da yawa wanda ya bar miliyoyin mutane cikin bukata tare da lalata amfanin gona da dabbobi. Kungiyoyin agaji sun yi gargadin cewa lamarin na iya kara tabarbarewa tare da yin kira da a gaggauta shiga tsakani a duniya
