News
Kotu ta bada dama Ajaka da SDP su binciki kayayyakin zaɓen Kogi
DAGA. MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Kotun shigar da korafin zaɓe ta Tribunal da ke zamanta a Lakoja ta amince da bukatar ɗan takarar gwamna, Murtala Ajaka na SDP na a ba su damar binciken kayayyaki da takardun zaɓen da aka gudanar a ranar 11 ga watan Nuwamba.
Mai shari’a Yusuf Ado Birnin-Kudu da ya bada wannan umarni, ya umarci hukumar zaɓe ta INEC ta bada wannan dama a cikin sa’o’i 24.
Kotu ta yan kewa mai yin lalata da almajirai ta dubura hukuncin ɗaurin rai da rai
Wannan umarni na zuwa ne bayan da lauyan masu korafi ya ce duk wani kokarinsu na samun damar nazartar kayayyakin zaɓen a Abuja da Lakoja ya gaggara.
Sai dai Mai shari’a Birnin-Kudu ya ce dole ne a bada wannan dama bisa tanadi na dokokin zaɓe da aka yiwa gyaran fuska a 2023.
Hukumar zaɓe ta INEC dai ta bayyana Ahmed Usman-Ododo a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan Kogin.
Ododo ya samu ƙuri’a 446,237, inda ya doke mai biye masa, Muritala Ajaka na jam’iyyar SDP, wanda ya samu ƙuri’u 259,052.
Dino Melaye na PDP ne ya zo na uku, inda ya samu ƙuri’u 46,362.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
