News
Zamu Dage Takunkumin Da Muka Saka Wa Kasar Nijar Akan Sharadi Guda -ECOWAS
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Mista Sidie Tunis, Kakakin Majalisar ECOWAS, ya ce za a dakatar da hukuncin da aka yanke wa Jamhuriyar Nijar, idan har gwamnatin soja ta saki Shugaba Mohamed Bazoum.
Shugaban majalisar ya ba da wannan tabbacin ne a lokacin da tawagar mutane 19 daga kungiyar ‘yan Afrika suka kai masa ziyarar ban girma a Abuja.
Babbar Magana: Ƙasar Jamus Ta Kirkiro Injin Kyankyasa Jarirai.
Ziyarar dai ita ce ta sanya majalisar ta goyi bayan dage takunkumin da aka kakabawa Nijar domin rage radadin da talakawa ke fuskanta a kasar.
Shugaban majalisar ya bukaci tawagar da ta saki Bazoum da iyalansa ba tare da wani sharadi ba tare da sanya wani dan gajeren lokaci don mayar da kasar bisa tsarin mulkin kasar.
Daily Post ta ruwaito cewa cewar Tunis, ba tare da la’akari da yunƙurin da ƙungiyar ta yi ba, ba a sami wani sakamako mai kyau ba tun bayan da gwamnatin mulkin soja ta kawar da zaɓen dimokuradiyya a Nijar.
-
Opinion7 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion7 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News5 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
