Connect with us

Business

Mun karya darajar Naira don mu samu shigowar ɗimbin daloli a hada-hadar Najeriya – Gwamnan CBN

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Gwamnan Babban Bankin Najeriya, CBN, Olayemi Cardoso, ya bayyana cewa darajar Naira ‘ta faɗi warwas”.

Advertisement

Cardoso ya bayyana haka a ranar Laraba, wurin Taron Majalisar Ƙolin Tattalin Arzikin Ƙasa (NESG) 2024.

Duk da dokar hana walwala da aka saka a Mangu, ana ci gaba da kisa da kone-kinen masallatai da Coci-coci

“Mu na da yaƙinin cewa a yanzu darajar Naira ya ragu sosai, kuma hakan wasu matakai ne da aka ɗauka a ɓangaren hada-hadar kuɗaɗe domin samar da farashin kankankan nan gaba kaɗan.

Advertisement

“Wannan tsari da muka bijiro da shi, zai taimaka wajen samar da farashin canjin kuɗaɗen ƙasashen waje wanda zai wanzar da daidaito,” inji Cordoso.

Kwanan nan dai darajar Naira ta faɗi warwas inda ake sayar da Dala 1 kan Naira Naira 1,372 a kasuwar ‘yan canji.

Advertisement

Premium Times ta ruwaito cewa a farashin gwamnatin tarayya kuma ana Dala 1 na Naira 878.

Cardoso ya ce yin hakan zai samar da daidaiton farashin canji, kuma zai samar da ƙarin samun daloli ta hanyar haɗa hannu da Ma’aikatar Harkokin Kuɗaɗe da kuma NNPCL domin ƙarfafa hada-hadar Dalaa cikin ƙasa.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending