News
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Gwamnoni Kan Ƙalubalen Da Nijeriya Ke Fuskanta
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI TUKUNTAWA
Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya ganawa da gwamnonin jihohi a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
Taron ya samu halartar mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima da mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu.
Taron wanda bai rasa nasaba da yanayin tsadar kayayyakin abinci da tabarbarewar tsaro a kasar, ya samu halartar gwamnoni sama da 27 da mataimakin gwamnan Bauchi.
Gwamnatin tarayya ta fara fitar da ton na hatsi iri-iri zuwa kasuwanni a wani bangare na kokarin samar da abinci, mai rahusa da sauki a fadin Najeriya.
Hakazalika, an dauki matakan cafke masu boye ahinci da nufin matsa wa al’umma ta hanyar hadin gwiwa tsakanin sojoji da sauran hukumomin tsaro.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
