News
Tsadar Rayuwa: Gwamnatin Legas Ta Bayyana Rangwamen Kashi 25 Cikin 100 Na Kayan Abincin
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gwamna Babajide Sanwo-Olu na jihar Legas ya kaddamar da kasuwannin da za su bayar da rangwamen kashi 25 cikin 100 ga mazauna jihar domin magance matsalar tattalin arziki da hauhawar farashin kayayyaki.
Gwamnatin jihar Legas ta sanar da hakan ne a ranar Asabar a cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai da dabaru, Gbenga Omotosho ya fitar.
Kotu Taki Amincewa A Saki Bayanan Kaddarorin Buhari Da Jonathan
Daily Post ta ruwaito cewa shirin mai taken ‘Ounje Eko’ kasuwannin abinci ana sa ran zai fara aiki a ranar Lahadi 17 ga Maris, 2024, a wurare 27, ciki har da Ikeja.
“An samo masu samar da hanyoyin biyan kuɗi masu zaman kansu da masu siyar da abinci kuma an zaɓi su a hankali don gudanar da aikin.
Advertisements
