Connect with us

News

Da Dumi-dumi: Majalisar Dattawa Ta Amince Da Kudirin Bai Wa Dalibai Rance A Matsayin Doka

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Majalisar Dattawa ta amince da kudirin bai wa dalibai rance a matsayin doka, biyo bayan tsallake karatu na uku da kudirin ya yi a ranar Laraba.

Advertisement

Wannan na zuwa ne biyo bayan nazari tare da amincewa da rahoton kwamitin majalisar mai kula da manyan makarantu, wanda shugaban kwamitin, Sanata Muntari Dandutse, ya gabatar a zauren majalisar a ranar Laraba.

Majalisa na neman yadda aka yi da Dala miliyan 300, da aka ciwo bashi da nufin ayyukan daƙile cutar zazzaɓin cizon sauro

Idan za a tuna a makon da ya wuce ne, kudirin ya tsallake matakin karatu na biyu a zauren majalisar.

Advertisement

LEADERSHIP HAUSA ta ruwaito cewa, a makon da ya gabata ne shugaba Bola Tinubu ya aike wa majalisar dattawa da ta wakilai wasikar kan bukatar soke shirin bai wa dalibai bashi.

Sabuwar dokar za ta inganta tsarin bayar da lamunin manyan makarantu, domin magance matsalolin dalibai da suka shafi daina zuwa makaranta, hanyoyin samun kudi da kuma hanyoyin biyan lamunin.

Advertisement

Matakin na Tinubu ya biyo bayan sanarwar dakatar da fara shirin bai wa dalibai rance na wucin gadi.

An kafa dokar ne domin bai wa daliban Nijeriya da ke manyan makarantun gaba da sakandare damar samun lamuni mai karancin ruwa don kammala karatunsu ba tare da sun samu tasgaro ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending