Connect with us

News

Hukumar EFCC Ta Sake Gurfanar Da Tsohon Gwamna, Dansa Bisa Zargin Almundahanar Naira Biliyan 29 A Gaban Kotu

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta sake gurfanar da tsohon gwamna Murtala Nyako da dansa Abdulaziz a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja ranar Alhamis bisa zargin almundahanar Naira biliyan 29.

An sake gurfanar da su a gaban kuliya bisa laifuka 37 da ake zargin sun aikata a lokacin da Mista Nyako ke gwamnan Adamawa.

Majalisar Wakilai Na Ƙoƙarin Yin Dokar Baiwa Masu Takaba Hutun Watanni Biyar

Sauran wadanda aka gurfanar dasu akwai Zulkifik Abba da Abubakar Aliyu.

Kamfanonin da ake zargin sun yi amfani da su wajen karkatar da kudaden—Blue Opal Limited, Sebore Farms & Extension Limited, Pagoda Fortunes Limited, Tower Assets Management Limited, da Crust Energy Limited — sun kasance gudaa biyar zuwa na tara.

Hukumar EFCC na tuhumar Mista Nyako, da dansa, da sauran wadanda ake tuhuma bisa zargin almundahanar kudi Naira biliyan 29.

Advertisement

EFCC ta yi zargin cewa wadanda ake tuhumar sun karkatar da kudade daga baitul malin Adamawa tsakanin watan Janairun 2011 zuwa Disamba 2014.

 

 

(NAN)

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending