News
Cutar Mashako ta kashe yara hudu a Kano
DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA
An samu bullar cutar Mashako yayin da ta kashe yara hudu a kauyukan karamar hukumar Mingibir ta jihar Kano.
Wata sanarwa da jami’in yada labarai na karamar hukumar Tasiu Yahaya Dadin-Duniya ya fitar, wanda aka turawa da gidan rediyon Arewa.
A cewar sanarwar “Yara hudu ne suka mutu sakamakon cutar Mashako sannan kuma yara 28 sun kamu da cutar a kauyukan Kwarkiya, Kuru, Kunya da Minjibir dake karamar hukumar Minjibir ta jihar Kano.
“Jami’in riko na karamar hukumar, Muhammad Yakubu Kunya, ya yi kira ga hukumomi da masu ruwa da tsaki da su gaggauta kai wa karamar hukumar Minjibir dauki domin kare lafiyar al’umma”.
Sanarwar ta ce Hakimin Karamar Hukumar ya kuma bukaci sarakunan gargajiya da malaman addinin Islama a cikin al’umma da su tashi tsaye wajen wayar da kan al’umma tare da yin addu’ar samun sauki.
A halin da ake ciki, ma’aikatar lafiya ta jihar ba ta tabbatar ko musanta bullar cutar ba.
