Connect with us

News

Muna Kokarin Ganin An Shawo Kan Matsalar Ruwa A Asibitin Kwararru na Murtala – Dr Nagoda

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Sakataren zartarwa na hukumar kula da asibitocin jihar Kano Dakta Mansur Mudi Nagoda ya yi kira da jama’a da su kara hakuri domin hukumar na kokarin ganin an shawo kan matsalar samar da ruwan sha a asibitin kwararru na Murtala Muhammad.

Dokta Nagoda ya yi wannan roko ne a lokacin da ya kai ziyarar gani da ido a ranar Larabar da ta gabata inda ya bukaci gwamnati ta samar da wasu hanyoyin da za a samu ruwa a Asibitin.

Cutar Mashako ta kashe yara hudu a Kano

Hakan na kunshe ne ta cikin wata Sanarwa da jami ar yada labarai ta Hukumar Samira Suleiman ta turawa da Jaridar Inda Ranka

Sanarwar ta karada cewa a halin yanzu, akwai rijiyoyin burtsatse guda 12 a cikin ginin amma saboda girma da kuma sauyin yanayi ruwan ba ya iya kaiwa.

Ya kara da cewa, “domin a samu saukin lamarin, za mu rika samar da tankokin ruwa guda biyu a kullum, 1 za a ajiye a sashin haihuwa, daya kuma a sashin yara .”

Advertisement

Bugu da kari, sakataren zartaswar ya yi kira ga gwamnatin jihar da ta samar da karin rijiyoyin burtsatse a cikin Asibitin

Haka zalika ya jaddada cewa hakan zai kara saukaka matsalar rashin isasshen ruwan sha a cikin Asibitin.

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending