News
‘Yan sanda sun kama mutum hudu dake safarar yara kanana a Kaduna
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta bayyana cewa jami’an ta sun kama wasu mutane hudu dake safarar yara kanana a jihar.
Jami’an tsaron sun kama Shehu Sani mai shekara 40, Tskan Isiaku mai shekara 43 da Hafsat Hussaini ‘yar shekara 24 duk dake suna zama a Ungwar Rimi a karamar hukumar Kaduna ta Arewa sannan da Angela Onazu dake zama a unguwar Sabon Tasha a karamar hukumar Chikun.
Yadda Gayyatar Da Jami’an Tsaro Suka Yi Da Sheikh Gumi Ta Gudana
Kamen da dakarun suka yi ya faru bayan sa’o’I 24 da dakarun suka kama wani sojan karya mai suna Ya’u Ja’afar dake damfarar mutane da kuma yi musu fashi da makami jihar.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar Mansur Hassan ya ce mutanen sun tabbatar wa jami’an tsaron cewa suna safarar yara kanana sannan dakarun sun ceto wata karamar yarinya mai suna Zainab mai shekara biyu daga hannun su.
Hassan ya ce mutanen sun yi bayanin cewa sukan kama yara kanana dake gararamba a titi da wadanda aka aike su su kadai ba tare da wani babba tare da su ba.
Ya yi kira ga iyaye da su rika sa ido suna kula da shiga da fitan ya’yan su domin kare su daga fadawa hannun mutane irin haka.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Ali Audu Dabigi ya ce jami’an tsaro za su ci gaba da kokarin wajen kare rayuka da dukiyoyin mutane a jihar.
-
News7 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News4 days agoKotu Ta Daure Wani Limamin Masallacin Juma’a Wata 1 Kan Tura Bidiyon Tsaraici Ga Matar Aure A Kano
-
News6 days agoƘalubalen Da Masu Ƙananan Sana’o’i Ke Fuskanta Saboda Ƙarancin Wutar Lantarki A Kano
