News
Gwamnan jihar Jigawa Malam Umar A. Namadi ya dakatar da kwamishinan ma’aikatar kasuwanci
DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA
Gwamnan jihar Jigawa Malam Umar A. Namadi ya dakatar da kwamishinan ma’aikatar kasuwanci kuma mamba a majalisar zartarwa ta jihar, Alhaji Aminu Kanta, kan zargin wasu badakaloli a shirin ciyarwa na watan Ramadana da gwamnatin jihar take yi.
Hakan ya zo ne a wata sanarwar da sakataren gwamnatin jihar, Malam Bala Ibrahim ya sanyawa hannu. Sanarwar ta bayyana hakan a matsayin yunkurin tabbatar da kididdigar da kuma lura da kudaden al’umar jihar ta Jigawa.
Mutum aƙalla 21 ne suka mutu sakamakon rikicin manoma da makiyaya a jihar Kogi
Jawabin ya bayyana umurnin gwamnan na sakataren gwamnatin ya mika takaddar dakatarwar a madadin gwamnatin jihar. Ya kara da cewa, An dakatar da kwamishinan ne bisa zarginsa da hannu wajen karkatar da kudaden ciyarwar buda baki a karamar hukumar Babura.
-
News17 hours ago
Jam’iyyar Labour Party Ta Yi Alkawarin Kafa Hukumar Kula Da Hayar Gidaje A Kano
-
News3 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News6 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
