Connect with us

News

Gwamnan jihar Jigawa Malam Umar A. Namadi ya dakatar da kwamishinan ma’aikatar kasuwanci

Published

on

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA 

Advertisements
Advertisements

Gwamnan jihar Jigawa Malam Umar A. Namadi ya dakatar da kwamishinan ma’aikatar kasuwanci kuma mamba a majalisar zartarwa ta jihar, Alhaji Aminu Kanta, kan zargin wasu badakaloli a shirin ciyarwa na watan Ramadana da gwamnatin jihar take yi.

Advertisements

Hakan ya zo ne a wata sanarwar da sakataren gwamnatin jihar, Malam Bala Ibrahim ya sanyawa hannu. Sanarwar ta bayyana hakan a matsayin yunkurin tabbatar da kididdigar da kuma lura da kudaden al’umar jihar ta Jigawa.

Advertisements
Advertisements

Mutum aƙalla 21 ne suka mutu sakamakon rikicin manoma da makiyaya a jihar Kogi

Jawabin ya bayyana umurnin gwamnan na sakataren gwamnatin ya mika takaddar dakatarwar a madadin gwamnatin jihar. Ya kara da cewa, An dakatar da kwamishinan ne bisa zarginsa da hannu wajen karkatar da kudaden ciyarwar buda baki a karamar hukumar Babura.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending