News
Kotu Ta Jingine Dakatarwar Da Aka Yi Wa Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa Abdullahi Ganduje
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Babbar Kotun Tarayya da ke Kano ta jingine dakatarwar da aka yi wa Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Ganduje, a mazabarsa.
Mai Shari’a Abdullahi Liman ya umarci shugabannin Mazaɓar Ganduje da ke Ƙaramar Hukumar Dawakin Tofa, kada su yi aiki da umarnin babbar kotun jihar na dakatar da shugaban jam’iyyar.
Umarnin Babbar Kotun Tarayyar na zuwa ne awa 24 da babbar kotun jihar ta amince da bukatar shugabannin mazabar ta dakatar da tsohon gwamnan jihar, saboda gwamnatin jihar mai ci na zarginsa da almundahana.
Alƙalin ya hana duk waɗanda umarnin kotun jihar ya shafa bin umarnin, har sai ya saurari ƙarar da Ganduje ya shigar gabansa ne neman adalci a saurari ɓangarensa.
Kotun ta kuma sanya ranar 30 watan nan na Afrilu domin sauraren buƙatar ta shugaban jam’iyyar kuma tsohon gwamnan Kano.
Shugabannin APC na mazaɓar Ganduje da lauyan shugaban na APC, Jazuli Mustapha, ya shigar ƙara su ne Haladu Gwanjo, Nalami Mai AC, Muhammadu Baiti, Danmalam Gata, Musa Lado, Laminu Sani Barguna, Umar Sanda, Auwalu Galadima da kuma Abubakar Daudu.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
