News
Hukumar da ke kula da gidan gyaran hali a Kano ta ce kashi 70 cikin 100 na fursunoni a jihar ke jiran shari’a.
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Hukumar kula gidajen gyaran hali reshen jihar Kano, ta ce karuwar masu jiran shari’a a cibiyoyin tsare masu laifi a jihar abu ne dake matukar tayar da hankali.
Wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar jihar, SC Musbahu Lawan ya sanya wa hannu, ta ce yawan nasu ya zama kalubale ga hukumar a jihar, inda ya ce adadin fursunonin da ke zaman wakafi ya rubanya na fursunonin dake daure a jihar.
Ya kuma kara da cewa fursunonin da aka yanke wa hukunci sun fi saukin gudanarwa domin an ba su damar shiga shirye-shiryen gyara daban-daban, wadda dama ce da masu jiran shari’a ba su da ita.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
