News
Gwamnatin Kano Ta Biya Wa Ɗalibai 1,740 Kuɗin Makaranta A Jami’ar Ilimi Ta Sa’adatu Rimi
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya biya wa sababbin dalibai 1,740 da suka samu gurbin karatu a jami’ar ilimi ta Sa’adatu Rimi da ke Kano.
Gwamna Yusuf ya bayyana haka ne a ranar Asabar a lokacin kammala yayin bikin maraba da zuwa na dalibai masu karatun digiri na daya a makarantar.
Almajirai Shida Sun Rasu Sakamakon Kamuwa Da Cutar Sankarau.
Leadership ta ruwaito cewa a shekarar 2023 ne Hukumar Kula da Jami’o’i ta Kasa (NUC) ta amince da daga darajar Kwalejin Ilimi ta Sa’adatu Rimi da ke Kumbotso a Jihar Kano zuwa jami’ar ilimi.
Ya ce gwamnatin jihar ta himmatu sosai wajen tallafawa bukatun ilimi na dalibai ba tare da la’akari da siyasa ba.
Ya ce gwamnatin jihar ta kuma ware kashi 30 cikin 100 na kasafin kudinta na shekarar 2024 ga ilimi, wanda hakan yasa aka samu kari daga shekarun baya.
Kwamishinan ilimi mai zurfi na jihar, Dr. Ibrahim Kofarmata, ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta yafe kashi 50 na kudaden makaranta na makarantun sakandire da manyan makarantun jihar domin samun saukin ilimi ga yara masu rauni.
Shugaban Jami’ar, Farfesa Yahaya Isa Bunkure, ya yabawa kokarin Gwamna Yusuf a kan harkar ilimi, ya kuma bayyana irin nasarorin da jami’ar ta samu, da suka hada da shirye-shiryen bunkasa ma’aikata, ayyukan bincike, da inganta ababen more rayuwa.
Bunkure ya ja kunnen daliban da su himmatu tare da yin azama da mayar da hankali a yayin da suke gudanar da karatunsu a jami’ar.
Bunkure, ya kuma samu lambar yabo ta ‘Fellowship’ daga Cibiyar Nazari ta (FNIP) saboda gudummawar da ya bayar a fannin da jajircewarsa wajen bincike da ilimi.
-
Opinion6 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion5 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News4 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
