News
Gwamnatin Jihar Kogi ta tabbatar da ceto ɗaliban da aka sace daga Jami’ar Confluence.
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Gwamnatin Jihar Kogi ta tabbatar da ceto wasu daga cikin ɗaliban da aka sace daga Jami’ar Confluence da ke jihar.
A wata sanarwa da gwamnatin ta fitar a ranar Lahadi, ta tabbatar da cewa ‘yan bijilanti da taimakon jami’an tsaro ne suka yi aikin ceto ɗaliban.
Darajar takardar kudin Naira ta ta sake komawa cikin mawuyacin hali
Gwamnatin ta ce wani ɗan bijilanti da jami’in hukumar DSS sun jikkata a yayin musayar wuta da masu garkuwar, amma a halin yanzu suna samun kulawa a asibiti.
Haka ma gwamnatin ta ce ɗaliban da aka ceton su ma an kai su asibiti domin duba lafiyarsu.
Advertisements
