Connect with us

News

Karin kudin wutar lantarki: Kungiyar Kwadago ta NLC Ta Lashi Takobin Zaman Dirshen A Gaban Ofishin Hukumar NERC A Gobe

Published

on

DAGA MUHAMMAD YASIR KABIRU 

Kungiyar kwadagon Nijeriya ta lashi takobin zaman dirshen a gaban ofishin hukumar NERC mai kula da farashin lantarki tare da rufe kamfanonin rarraba lantarki har sai sun janye sabon karin kudin lantarkin da suka yi a baya-bayan nan.

Advertisement

Daily Post ta ruwaito cewa Karin kudin wutar lantarki: NLC za ta dauko DISCOs, ofisoshin NERC a ranar Litinin

Shugaban Rasha Vladimir Putin Ya Sauke Ministan Tsaron Ƙasar Sergei Shoigu Daga Muƙaminsa

 

Advertisement

Kungiyar kwadagon Nijeriya ta lashi takobin zaman dirshen a gaban ofishin hukumar NERC mai kula da farashin lantarki tare da rufe kamfanonin rarraba lantarki har sai sun janye sabon karin kudin lantarkin da suka yi a baya-bayan nan.

Kungiyar ta NLC ta ce mambobinta rufe kamfanonin rarraba wutar  lantarki  DISCOs, a duk fadin Najeriya.

Advertisement

Umarnin ya biyo bayan taron kwamitin  CWC, a ranar 30 ga Afrilu, 2024.

Wata sanarwa mai dauke da sa hannun mukaddashin sakataren kungiyar NLC, Chris Uyot, ta ce: “An shirya rufewar ne  a duk faɗin ƙasar a ranar Litinin, 13 ga Mayu, 2024.”

Advertisement

Kungiyar kwadagon ta rubuta wasikar zanga-zanga zuwa hedkwatar NERC inda ta ba da wa’adin ranar 12 ga Mayu, 2024 cewa NERC ta sauya karin kudin wutar lantarki ko kuma a dauki matakin gaggawa.

Kungiyoyin sun bayar da misali da halin da ake ciki na cewa matakin NERC zai ingiza al’umma sabida Tsadar rayuwa

Advertisement

Sun bayyana cewa karin kudin da  aka sanar ba wai ya sabawa tsarin da doka ba, har ma da take hakkin ‘yan Najeriya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending